Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ma’aikatan jinya 18 sun kamu da Corona a Kano

Published

on

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta jihar Kanoano tace ma’aikatan su 18 ne suka kamu da cutar Covid-19 ba tare da sun sani ba a yayin da suke tsaka da ayyukan ceton rayukan al’umma.

Shugaban kungiyar Ibrahim Maikarfi Muhammad ne ya bayyana hakan a zantawarsa da wakilinmu Abba Isah Muhammad, inda ya ce sun yiwa ma’aikatansu 188 gwajin cutar Corona wanda sakamakonsu ya tabbatar da cewa mutum 18 na dauke da cutar.

Maikarfi Muhammad yace ma’aikatansu ne kan gaba wajen saurin kamuwa da cutar matukar gwamnati bata samar musu da isassun kayan kariya ba.

Karin labarai:

An sallami mutum 6 da suka warke daga Corona a Kano

Corona ta hallaka mutane 13 a Kano

Wannan yana zuwa ne kwana guda bayan da kungiyar likitoci ta kasa reshen jihar Kano ta sanar da cewa mambobinta 34 ne suka kamu da cutar ta Covid-19 a Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!