Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Lafiya: Mata na fuskantar barazanar kamuwa da cutuka lokacin al’ada

Published

on

Wata kwararriyar likitar mata a asibiti Amiu Kano Dakta Zainab Datti Ahmad ta ce, rashin tsaftace jiki lokacin al’ada ga Yaya Mata shi ne ke haifar musu da bakin cututtuka a wannan lokaci.

Dakta Zainab Datti Ahmad ta bayyana hakan yayin Taron wayar da kan Mata kan yadda za su kula da tsaftar jikin su musamman a lokacin jinin al’ada a wani bangare na makon bikin al’ada da ake gudanarwa wanda Gidauniyar Widi Jalo Foundation ta gudanar.

A cewar likitar wajibi ne ga matan da suke yin al’ada duk lokacin da za su shiga bandaki ya zamana suna tsaftaceshi tahanyar amfani da sinadaren dake kashe cutuka.

Haka Kuma ta ce, duba da rashin kudi a hannun Mutane mace za ta iya amfani da Toka wajen wanke bandake idan za ta shiga, tare da yin amfani da Lalle da Ruwan da aka jika Toka da Kuma Alimun wajen wanke jiki.

Da yake jawabi shugaban Gidauniyar ta WIDI JALO Alhaji Abubakar WIDI, da Jami’ar Gidauniyar a nan Kano Hajiya Bilkisu Hamisu Mai Iyali tayi magana a madadin SA ta ce duba da wahalar da Mata suke Sha lokacin jinin al’ada na Rashin abin da za su kula da kan su yasa suka shirya musu bitar.

Yayin bitar ta wuni guda Likitoci da daliban kiwon Lafiya daga Asibitocin jihar Kano da dama ne suka gabatar da jawabai kan yadda Mata za su kula da kansu lokacin jinin al’ada.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!