Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Lauyan Barcelona na yunkurin dakatar da cinikin Lionel Messi

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta shigar da korafi a gaban hukumar tarayyar Turai a yankurin dakatar da Lionel Messi daga ficewa daga kungiyar.

Lauyan dake wakiltar Barcelona ne ya gabatar da korafin yana kalubalantar damar da PSG ke da ita na ka’idar kudaden da zata iya kashewa wajen sayan dan wasa bai kai darajar na Barcelona.

A yau Litinin ne 9 ga watan Augusta PSG ke dakon zuwan Messi don ci gaba da taka leda a kungiyar.

Messi ya tabbatar da ficewarsa daga Barcelona bayan da ya shafe shekaru 21 a kungiyar, yayin da yake bankwana a ranar Lahadi 8 ga watan Augustan 2021.

Ya ce, a shirye yake da ya rage albashinsa da kaso 50 domin ya ci gaba da zama a kungiyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!