Connect with us

Labarai

Majalisar Dattawa na neman hana shigo da Yaduddukan Kasashen Waje

Published

on

Majalisar dattijai

Majalisar Dattawa Ta Nemi Haramta Shigo da Yaduddukan Kasashen Waje Domin Farfado da Masana’antar Yadi

Majalisar Dattawan Najeriya ta bukaci Gwamnatin Tarayya da ta haramta shigo da yaduddukan kasashen waje gaba daya, domin farfado da masana’antar yadi ta cikin gida da kuma bunkasa noman auduga a fadin kasar nan.

Haka kuma, majalisar ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta hannun Ma’aikatun Noma da Kasuwanci da Zuba Jari da su dauki matakan gaggawa domin dawo da martabar masana’antun yadi a Najeriya, musamman a yankin masana’antu na Kaduna zuwa Kano.

Sanatocin sun bayyana cewa farfado da wadannan masana’antu zai samar da dubban ayyukan yi ga matasa, tare da taimakawa wajen rage matsalar rashin aikin yi da kuma kalubalen tsaro da ke addabar kasar.

Wannan kuduri ya samu amincewar majalisar ne bayan tattauna wata bukata mai taken “Gaggawar Farfado da Masana’antun Yadi a Najeriya, Musamman a Yankin Kaduna da Kano”, wadda Sanata Sunday Katung na jam’iyyar APC mai wakiltar Kaduna ta Kudu ya gabatar, tare da goyon bayan wasu sanatoci daga jam’iyyu daban-daban.

Sanatocin sun jaddada cewa dawo da masana’antar yadi zai taimaka wajen farfado da tattalin arzikin Najeriya, bunkasa masana’antu na cikin gida, da kuma rage dogaro da kayayyakin da ake shigo da su daga kasashen waje.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!