Connect with us

Labarai

Sojoji sun ceto mutane 360 da ’yan ta’adda suka sace a Borno

Published

on

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai tare da dakaru na musamman sun ceto mutane 360, galibinsu mata da kananan yara, da ’yan ta’adda suka sace daga garin Ngoshe a  karamar hukumar Gwoza ta jihar Borno.

Kwamandan rundunar, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, ya ce an gudanar da samamen ne a yankin tsaunukan Mandara a ranar 6 ga Yuni, inda aka samu nasarar kubutar da wadanda aka sace tun bayan harin da aka kai wa al’ummar Ngoshe a watan Maris.

Sai dai ya ce jarirai biyu sun rasu yayin aikin ceton sakamakon wahalar hanya. An kuma kai wadanda aka ceto asibiti domin kula da lafiyar su kafin a hada su da iyalan su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!