Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Majalisar dinkin duniya ta yi Allawadai da harin da ‘yan bindiga a jihar Kaduna

Published

on

Majalisar dinkin duniya ta yi Allawadai da harin da ‘yan bindiga suka kai a wani kauye da ke yankin karamar hukumar birnin Gwari a jihar Kaduna wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.

 

Babban sakatare Janar na majalisar Antonio Gutteres ne ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa Stephane Dujarric ya fitar jiya a shalkwatar hukumar da ke birnin Washington DC.

 

Antonio Gutteres ta cikin sanarwar dai ya kuma ce ya zama wajibi hukumomi a kasar nan su zakulo wadanda ke da hannu cikin lamarin domin gurfanar da su gaban kuliya.

 

Sanarwar ta kuma ruwaito Antonio Gutteres na jajantawa iyalai da ‘yan uwan wadanda lamarin ya shafa.

 

A ranar Asabar din makon jiya ne dai wasu ‘yan bindiga suka hallaka mutane sama da saba’in a kauyen Gwaska da ke yankin karamar hukumar birnin Gwarin jihar Kaduna.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!