Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Abin da ya sanya Majalisar dinkin duniya ta ce an kashe manoma 110 a Borno

Published

on

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce kimanin mutane 110 aka kashe a harin da ake tunanin ƴan Boko Haram ne suka kai wa manoma a jihar Borno.

Hakan na cikin wata sanarwa da mai kula da ayyukan jin-ƙai na Majalisar Edward Kallon ya fitar, inda ya kira harin da mummunan tashin hankali.

Sai dai sanarwar da gwamnatin Borno ta fitar bayan jana’izar mutanen, ta ce mutane 43 ne suka hallaka a harin.
Bayan kisan, gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya yi kira ga matasa da su shiga aikin ƴan banga ko sa-kai domin yaƙi da ta’addanci.

A ranar Asabar ne aka samu rahotannin da ke cewa wasu da ake tunanin mayaƙan Boko Haram ne sun shiga gonaki inda suka kashe fiye da mutum 40.

Lamarin ya faru ne a yankin Koshebe na Zabarmari da ke cikin Ƙaramar Hukumar Mafa ta jihar Bornon.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!