Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokoki ta yarje wa Abba Gida-Gida ciyo bashin Biliyan 4

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano, ta sahale wa Gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf, damar karɓar bashi maras ruwa na Naira biliyan huɗu daga Babban bankin ƙasa CBN.

Majalisar, ta sahale ciyo bashin ne a zamanta na yau Juma’a biyo bayan wasiƙar da gwamnan ya aike wa majalisar wadda shugabanta Jibril Isma’il Falgore ya karanta jim kaɗan bayan da gwamnan ya gabatar da ƙunshin Kasafin kuɗin baɗi.

Ta cikin wasiƙar gwamnan ya ce, zai yi amfani da bashin ne wajen ƙarasa aikin samar da tashoshin lantarki mallakin jihar Kano a madatsun ruwa na Challawa da Tiga.

Da yake ƙarin haske kan wasiƙar, shugaban masu rinjaye na majalisar Alhaji Lawan Hussaini Chediyar ƴan Gurasa, ya buƙaci mambobin majalisar da su amince da ciyo bashin kasancewarsa maras ruwa kuma aikin zai taimaki al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!