Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta amince da sabuwar dokar ma’adanai

Published

on

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta amince da sabuwar dokar hakar ma’adanai a Jihar, wadda ta ba da damar haka tare da karbar kudaden haraji daga masu hakar ma’adanan.

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoton da kwamitin harkokin kudi da tsare-tsare na majalisar ya yi a zamanta na jiya alhamis.

Da yake gabatar da rahoton, shugaban kwamitin Alhaji Sama’ila Salihu Biu, ya ce, kafin gabatar da rahoton sai da suka tattauna da masu ruwa da tsaki da lamarin ya shafa, tare da fito da shawarwari da al’amuran da ya kamata a yi wa duba na tsanaki musamman a harkokin karbar haraji.

Dokar dai ta yi tanadin cewa, dukkan wuraren hakar ma’adanan za su kasance karkashin mallakin gwamnatin jihar, don haka gwamnatin jihar na da ikon karbar kudaden haraji daga masu hakar ma’adanai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!