Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar Kano ta nemi Ganduje ya gina tituna a karamar hukumar Minjibir

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta buƙaci gwamnatin Jihar Kano da ta gina titi a wasu hanyoyin da ke karamar hukumr Minjibir musamman hanyar da ta tashi daga garin Cheɗi ta bi ta Yola zuwa Ladin Ɗandake, ta haɗe da wata hanya da ke sada karamar hukumar, da hanyar da ke zuwa ƙaramar Ɓaɓura ta Jihar Jigawa.

Buƙatar hakan dai ta biyo bayan ƙudurin da dan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Minjibir kuma mataimakin Shugaban masu rinjaye na majalisar Alhaji Tasi’u Ibrahim Zabainawa ya gabatar a zaman majalisar na yau.

Alhaji Tasi’u Ibrahim Zabainawa ya ce al’ummar garuruwan na fama tarin matsaloli sakamakon rashin hanyar, duk kuwa da cewa akwai wata babbar kasuwa mai tsohon tarihi a yankin.

Da yake goyon bayan ƙudurin dan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Sumaila Alhaji Zubairu Hamza Massu, ya ce ya kamata gwamnatin jiha ta yi gaggawar kaiwa al’ummar ƙaramar hukumar ɗauki.

Wakilinmu na majalisar dokokin ta Kano Auwal Hassan Fagge ya rawaito cewa bayan kammala zamanta na yau, majalisar ta ɗage ci gaba da zama har zuwa makon gobe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!