Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Shugaban Buhari ya karbi wasu shugabannin jam’iyyar APC a fadar Asorok

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karbi wasu shugabannin jam’iyyar APC a wajen wata liyafar cin abinci a fadar Asorok da ke Abuja a daren jiya.

Shugaban jam’iyyar APC na kasa Chief John Odigie Oyegun ne ya jagoranci ‘yayan jam’iyyar zuwa wajen liyafar cin abincin.

Sauran ‘yayan jam’iyyar ta APC da suka halarci liyafar cin abincin sun hada da: sakataren jam’iyyar Mai Mala Buni, da tsohon gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da tsohon gwamnan Sokoto Aliyu Magatakarda Wamakko da tsohon gwamnan jihar Abia Uzor Orji Kalu da kuma sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha.

Sauran sune: mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa Injiniya Segun Oni da tsohon gwamnan jihar Enugu Sullivan Chime da Olorogun O’tega Emerhor da tsohon gwamnan jihar Nassarawa Sanata Abdullahi Adamu da kuma Alhaji Abubakar Kawu Baraje.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!