Labarai
Majalisar Koli ta Shari’a ta kalubalanci matakin kafa ‘Yan-Sandan Jihohi

Majalisar Koli ta Shari’a a kasar nan SCSN ta bayyana cewa duk da muhimmancin inganta tsaro, bai kamata a ɗauki kafa ‘Yan Sandan Jihohi a matsayin mafita kai tsaye ga matsalolin tsaron ƙasar ba.
Ta cikin warta sanarwar da Sakatare Janar na Majalisar, Nafiu Baba Ahmad, ya fitar a ranar 30 ga Yulin 2026, majalisar ta ce matsalolin tsaro sun samo asali ne daga ƙarancin kuɗaɗe, cin hanci, ƙarancin jami’ai, rashin ingantattun kayan aiki, raunin tattara bayanan sirri da kuma rashin kyakkyawar haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro.
Majalisar ta buƙaci a fara gyara da ƙarfafa hukumomin tsaron da ake da su, tare da nuna damuwa kan yadda ake gaggauta yin gyaran kundin tsarin mulki domin kafa ‘Yan Sandan Jihohi ba tare da cikakkiyar tattaunawa da ‘yan ƙasa ba.
You must be logged in to post a comment Login