Connect with us

Labarai

Majalisar Wakilai ta amince da kudirin kafa ’Yan Sandan jihohi

Published

on

Majalisar Wakilai ta amince da kudirin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya da zai bai wa jihohi damar kafa rundunar ’yan sandansu, bayan da mambobi 289 cikin 290 da suka halarci zaman suka kada ƙuri’ar goyon baya. Haka kuma Majalisar Dattawa ta yi karatu na biyu kan kudirin, lamarin da ke nuna cewa an samu gagarumin ci gaba wajen kokarin sauya tsarin aikin ’yan sanda daga hannun gwamnatin tarayya kaɗai zuwa haɗin gwiwa da jihohi.

Kudirin ya tanadi kafa rundunonin ’yan sandan Tarayya da na Jihohi tare da fayyace ayyukan kowanne bangare. An kuma shimfiɗa ƙa’idojin da jihohi za su bi kafin su fara gudanar da rundunonin nasu, tare da kafa hanyoyin sa ido da kariya domin tabbatar da cewa ba a yi amfani da rundunar wajen muradun siyasa ko cin zarafin jama’a ba.

Masu goyon bayan kudirin sun bayyana cewa tsarin zai taimaka wajen inganta tattara bayanan sirri, saurin kai dauki da kuma ƙarfafa tsaron al’umma saboda jami’an jihohi sun fi sanin yankunansu. Sai dai wasu masu adawa sun nuna damuwa kan batun kuɗaɗen gudanarwa da yiwuwar samun sabani tsakanin rundunonin Tarayya da na Jihohi, duk da cewa ana ganin kudirin ya kawo Najeriya kusa da kafa ’yan sandan jihohi a hukumance.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!