Labarai
NLO ta sanar da ranar fara gasar matasa ‘yan ƙasa da shekaru 19

Hukumar dake shirya gasar ƙananan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa ta ƙasa (NLO) ta sanar da cewa za a fara gasar matasa ‘yan ƙasa da shekara 19 a ranar Asabar, 15 ga watan nan da muke ciki na Agusta.
Hukumar ta bayyana hakan ne ta cikin sanarwar da ta fitar a shafukanta na Internet, inda ta ce an tanadi filayen wasa 16 da za su karɓi bakuncin gasar.
Hukumar ta NLO ta kuma sanar da cewa ranar Juma’a, 7 ga Agustan 2026 ce za ta kasance ranar ƙarshe ta rajistar ‘yan wasa, tare da umartar dukkan ƙungiyoyin da za su shiga gasar da su kammala rajistar ‘yan wasansu ta shafinta na yanar gizo.
Hukumar ta ƙara da cewa duk ƙungiyar da za ta fafata a gasar dole ne ta kasance tana da alaƙa da hukumar ƙwallon ƙafa ta jiharta, sannan ta biya kuɗin rajistar shekara-shekara da hukumar NLO ta kayyade.
Ta yi gargaɗin cewa duk ƙungiyar da ta kasa cika waɗannan sharuɗɗa za a ɗauke ta a matsayin wadda ta janye daga gasar.
You must be logged in to post a comment Login