Labarai
Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci a yi gaggawar kafa ‘yan sandan jihohi

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro su kara kaimi wajen ceto dalibai da malamai da aka sace a jihohin Oyo da Borno, tare da sake jaddada bukatar kafa ’yan sandan jihohi domin magance matsalar tsaro da ke addabar Nijeriya.
Jaridar Premium Times, ta rawaito cewa majalisar ta faɗi haka ne bayan tattauna wasu kudurori biyu da suka shafi sace-sacen dalibai da hare-haren da ake kai wa al’umma a sassan kasar nan.
Dan majalisar mai wakiltar mazabar Ogbomoso ta Arewa da Ogbomoso ta Kudu a jihar Oyo, Hon. Olamijuwonlo Alao-Akala, ya bayyana damuwarsa kan yadda hare-haren ’yan bindiga ke karuwa a yankunan Ogbomoso da Orire, yana mai cewa hakan ya zama babbar barazana ga rayuka da harkar ilimi.
You must be logged in to post a comment Login