Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar wakilai ta buƙaci a katse layukan sadarwa a Sokoto

Published

on

Majalisar wakilan kasar nan ta yi kira ga hukumar sadarwa NCC da ta dakatar da ayyukan sadarwa a jihar Sakoto.

Majalisar ta buƙaci NCC din da ta rufe ayyukan sadarwa a wasu Kananan hukumomin da suka hadar da Bodinga, Dange-Shuni, da Tureta a Jihar Sakoto saboda rashin tsaro.

Majalisar ta kuma yi kira ga sojoji da su tura jami’an su zuwa sansanonin da abin ya shafa don dakile ‘yan fashi da sauran masu aikata laifuka a yankin.

Wannan dai ya biyo bayan kudurin da dan majalisa mai wakiltar Bodinga Dange-Shuni Tureta, Balarabe Kakale ya gabatar.

Kakale ya ce, an samu karuwar tabarbarewar yanayin tsaro a kananan hukumomi uku na mazabarsa a cikin makwannin da suka gabata, kuma hakan ya haifar da kisan gilla ga al’ummar yankunan Galma, Dutse, Buolere, da Hausare a gundumar wababe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!