Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Malam Abduljabbar ya sake gindaya sharuɗan tuba

Published

on

 

Sheikh Abduljabbar Kabara ya sake gindaya sharuɗa ga malaman Kano, matuƙar da gaske suna so ya tuba daga abin da suke zargin sa.

Malamin ya ce, har yanzu ba a gamsar da shi da hujjojin da suka fi nasa ba.

Ya ce, “Ya za a yi na yi karatu awa biyu zuwa uku ina warware matsala, sannan a yanko minti biyar a ce sai na ce kaza cikin minti goma.

“Me ya hana a ɗauko karatun gaba ɗaya a tattauna?”.

Ya ƙara da cewa, indai za ayi haka, to ba a biyo hanyar da ake cewa, ana so na tuba ba, ba da gaske ake ba, ba kuma gyara ake cewa ana so ba.

Malamin ya kuma ƙalubalancin malaman da su zo a biyo duk karatukan da yake yi, ba wai a gutsuro wata gaɓa ba.

Sheikh Abduljabbar ya ce, duk kalaman da ake jingina masa cewa yayi ɓatanci ba gaskiya bane, hassalima shi ƙoƙarin kare musulunci ya ke.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!