Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Rashin tsaro: Mun rasa malamai sama da ɗari 8 a Arewa maso Gabas

Published

on

Ƙungiyar malaman makarantu ta ƙasa NUT ta ce, sama da malamai ɗari takwas ne suka rasa rayukan su sanadiyyar ayyukan ta’addanci a sassan ƙasar nan.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa Dakta Nasir Idris ne ya bayyana hakan, a zantawar sa da manema labarai a ƙarshen mako.

Shugaban yayi barazanar cewa, za su janye malamai da ɗalibai a makarantun da ba su da isasshen tsaro a faɗin ƙasar nan.

Dakta Nasir Idris, ya kuma ce akwai malamai da ɗalibai da dama da aka sace a sassan ƙasar nan, musamman ma a arewa maso gabashin kasa nan a shekarar 2021.

Ya kara da cewa fara aiwatar da sabon tsarin biyan albashi zai taimaka matuka wajen farfado da tattalin arzikin kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!