Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Mambobin Majalisar Dokokin Kano za su yi wa Ɗan Adaidaita Sahu karo-karon kuɗi

Published

on

Mambobin majalisar dokokin jiha Kano su 40 za su yi karo-karon kuɗi cikin albashinsu domin bai wa matashin nan mai sana’ar Tuƙa babur ɗin Adaidaita Sahu Auwalu Salisu da aka fi sani da Ɗanbaba, wanda ya tsinci kuɗi kimanin naira miliyan 18 a nan Kano tare da mayar da su ga mamallakinsu.

Shugaban majalisar Jibril Isma’il Falgore, ne ya bayyana hakan yayin zaman majalisar na yau Litinin, biyo bayan ƙudurin ƙashin kai watau Motion of Personal Explanation da ɗan Majalisar Doguwa Alhaji Salisu Ibrahim Muhammad ya gabatar.

Da ya ke gabatar da ƙudurin, ɗan majalisa na Doguwa, ya buƙaci majalisar har ma da ƙungiyoyin kishin al’umma da masu rajin tabbatar da aikata gaskiya da su karrama wannan matashi mai shekaru 21 da ya yi abun a taɓa duk da irin matsananci hali da suke ciki a gidan su.

Da ya ke mayar da martani kan abun a yaba da matashin ya nuna, shugaban majalisar Jibril Isma’il Falgore, ya bayyana cewa majalisar za ta gayyaci Ɗanbaba inda zai yi musabaha da shi tare da yin karo-karo don tallafa masa.

Ɗaukacin mambobin majalisar sun amince da ƙudurin tare da taba wa matashin wanda rahotonni suka tabbatar da cewa tun da jimawa ya daina zuwa makarantar Sakandaren Kawaji da ke yankin ƙaramar hukumar Nassarawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!