Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun gano ƴan kwangilar layin dogo na yin aiki da karfe mara inganci Minista

Published

on

Gwamnatin tarayya, ta bayyana matsalar rashin rashin tsaro a matsayin dalilin da ya sanya ba za ta faɗi wa’adin kammala aikin layin dogon da ya tashi daga Kano zuwa Kaduna ba.

Ministan sufuri Alhaji Sa’idu Ahmad Alƙalin, ne ya bayyana hakan yayin da ya ke duba aikin da kuma yadda za a kammala aikin a kan lokaci domin sauƙaƙa harka sufuri.

Ministan ya ce, yanzu haka gwamnati za ta mayar da hankali wajen ganin an kammala aikin cikin gaggawa, sai dai rashin tsaro ya sanya dole a riƙa bi a hankali da kuma samar da ingantattun kayan ayyukan da ake aiki da su.

Haka kuma ya ce, yanzu haka ya gano wani ƙarfe da ƴan kwangilar ke yin aiki da shi a kan titin layin dogon wanda ba shi da inganci kuma baida inganci kuma ɓata gari za su iya zuwa su kwance shi, don haka ya umarci ƴan kwangilar da su gaggauta canja shi su saka wanda ba za a iya cirewa ba bayan an kammala aikin.

Ministan sifurin ya ce, wannan aikin zai kasance an kammala shi da wuri kasancewar layin dogon zai wuce ne har zuwa birnin Maraɗi na jamhuriyar Nijar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!