Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Manchester United ta nada Ralf Rangnick a matsayin mai horar da kungiyar na riƙon kwarya

Published

on

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester United, ta sanar da nada tsohon mai horar da tawagar Schalke 04, dan ƙasar Jamus (Germany) Ralf Rangnick, a matsayin mai horar da ƙungiyar na wucin gadi (Interim).

Mai shekaru 60, Rangnick zai jagoranci ƙungiyar na tsawon wata 06, a matsayin mai horar da ƙungiyar na wucin gadi zuwa watan Mayu na shekarar 2022, kamar yadda sanarwar da ƙungiyar ta fitar a shafinta na Internet.

A makon da ya gabata, rahotanni suka mamaye kafafen yada labarai na Ingila da Jamus, na cewar Rangnick ya cimma matsaya da tawagar ta United , na horar da ƙungiyar , da kuma yiwuwar aiki da ita a gaba bayan kammala wa’adin sa, a matsayin mai bada shawara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!