Connect with us

Tsaro

Manyan hafsoshin tsaro sun isa Maiduguri domin aikin wanzar da zaman lafiya

Published

on

Manyan hafsoshin tsaron kasar nan sun isa birnin Maiduguri, domin ƙara ɗaukar matakan da za su inganta tsaro a yankin Arewa maso Gabas, bayan da mayaƙan Boko Haram suka ƙaddamar da manyan hare-haren Bama-bamai a jihar.

 

Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar O.O. Oluyede, tare da Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shuaibu, ne suka isa birnin a wani muhimmin aiki na tsaro.

 

Ziyarar tasu na zuwa ne bayan umarnin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar, inda ya buƙaci shugabannin tsaro su mayar da cibiyar tsarawa da gudanar da ayyukan tsaro zuwa Maiduguri.

 

Ana ganin wannan mataki a matsayin wani sabon yunƙuri na ƙarfafa yaƙi da matsalolin tsaro da ke addabar yankin.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!