Connect with us

Labarai

Masarautar Bichi ta nemi hadin kan kungiyoyi domin samar da Lantarki mai amfani da hasken Rana

Published

on

Majalisar Masarautar Bichi, ta bukaci da ta hada hannu da kungiyoyi masu zaman kansu da nufin samar da wadataccen hasken wutar lantarki a wasu yankunan masarautar ta hanyar amfani da hasken rana.

Mai martaba sarkin Bichi Alhaji Nasiru Ado Bayero OFR, ne ya mika bukatar hakan lokacin da yake bude aikin tashar wutar lantarki mai amfani da hasken rana a kauyen ‘Yal’lami da ke yankin karamar hukumar Bichi.

tun da fari dai, Majalisar Masarautar ta Bichi da hadin gwiwa wani kamfani ne suka gudanar da ya aikin wanda ya lashe miliyoyin naira.

Mai martaba Sarkin Bichi Alhaji Nasiru Ado Bayero OFR ya kara da cewa, tasha za ta samar da wutar da za ta taimaka wa al’umma matuka, don haka akwai bukatar sake samar da karin wata domin ci gaban al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!