Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Masu ciwon sikari su rinka sahur da abinci mai nauyi-Likita

Published

on

Wani kwararre likitan kula da masu cutar ciwon sikari Dr Ibrahim Dan-Jumai Kura ya bukaci masu cutar da su riga yin sahur da abinci mai nauyi don gujewa shiga matsala a yayin watan Ramaddan mai zuwa.

Dr Ibrahim Dan-Jumai Kura ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan gidan Radio Freedom, wanda ya maida hankali kan hanyoyin da masu wancan cutar za su bi don kiyaye lafiyar su.

A cewarsa, masu cutar Sikari su kuma riga yawaita shan ruwa duba da irin zafin da ake fama da shi a wannan lokacin.

Shi ma wani kwararren Likita a fanni abinci mai gina-jiki Malam Yusuf Salish Kura, ya ce yana da kyau mai azumi ya fara cin kayan itatuwa da zarar ya bude baki, daga bisani sai a sha abu mai dan-dumi-dumi don inganta lafiya.

Masanan dai sun bukaci al’ummar musulmai da su gujewa amfani da ruwa mai sanyi da kuma rage zama cikin sanyi sosai kare kare lafiya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!