Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

An yiwa daya daga yaran Kano da aka sace fyade

Published

on

Daya daga cikin yara tara da aka ceto a garin Onitsa dake jihar Anambra, ta fuskanci cin zarafi na fyade a hannun wanda suka sace ta, kamar yadda cibiyar da ke lura da wadanda suka fuskanci matsala ta fyade ta bayyana.

 

Manajan cibiyar Nasiru Garko ne ya bayyanawa jaridar Kano Focus cewar, bayan duba daya daga cikin yaran yar shekara 10 domin tabbatar da ba ta dauke da wasu cutuka da ake samu ta hanyar cin zarafi.

 

Ya ce yarinya ta bayyana cewar an aikata fyade da ita sau da dama daga hannun wanda ya sace ta.

Malam Garko wanda likita ne ya tabbatar da faruwar hakan.

Yaran da aka sace sun kaiwa Ganduje ziyara

 

An dai kafa wannan cibiyar ne a karkashin kulawar asibitin kwararru na Murtala Muhammad dake nan Kano.

 

Kawun yarinyar wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce babban burinsu shine a bi musu hakkinsu dangane da garkuwa da akayi da yarsu.

 

Ya na mai cewa zasu tattaua don ganin an shigar da kara akan cin zarafi da aikata fyade da aka yi akan ‘yar ta su.

 

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!