Connect with us

Kiwon Lafiya

Ministan harkokin cikin gida ya bayyana takaici yadda ya tsinci tarin kalubalen a yayin aiki da tsohon sufeton janar ‘yan sanda

Published

on

Ministan harkokin cikin Gida Laftanal janar Abdurraham Dambazau ya bayyana takaicin sa kan yadda ya tsinci tarin kalubale lokacin da yake aiki da tsohon sufeto janar na ‘yan’sandan kasar nan Ibrahim Kpokun Idris lokacin yana bakin aikin sa.

Danbazau ya bayyana hakan ne jiya lokacin lokacin da ya ke karbar bakuncin sabon Sufeton yan’sandan Mohammad Adamu a birnin tarayya Abuja.

Ya kuma ce, yana fatan Sabon Sufeton ‘yan’sandan Muhammad Adamu ba zai yi koyi da irin dabi’un tsohon sufeton ‘yan’sandan kasar nan ba, a cewar sa  a shirye ya ke don ganin sun bashi gudunmawa wajen tabbatar da tsaro a fadin kasar nan.

Laftanar janar Dambazau ya ce a wannan lokacin za suyi kokari don dawo da dangantar dake tsakaninsu da rundunar yan’sanda kasar nan don yin aiki  kafada da kafada da hukumin tsaro  kamar yadda yake fuskantar matsalar tsaron  a fadin kasar nan.

Da yake jawabi sabon Sufeton ‘yan’sandan Muhammad Adamu yayi alkawarin canja yadda yake gudanar da aikin sa  tare da kawo gyara akan harkokin tsaron kasar nan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!