Labarai
Tinubu ya bukaci likitocin Najeriya da ke waje su dawo gida

Shugaba Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga likitocin Najeriya da sauran ƙwararrun ma’aikatan lafiya da ke aiki a ƙasashen waje da su dawo gida domin bayar da gudunmawarsu wajen inganta harkokin lafiya a ƙasar.
Tinubu ya bayyana hakan ne lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar Ƙungiyar Likitocin Najeriya da ke ƙasashen waje tare da shugaban Hukumar ‘Yan Najeriya Mazauna Ƙasashen Waje (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, a Abuja.
Ya ce Najeriya na buƙatar ilimi, ƙwarewa da gogewar ‘yan ƙasar da suka yi fice a ƙetare domin gina ingantaccen tsarin kiwon lafiya da zai amfani kowa da kowa.
Shugaban ya yaba wa likitoci ƙasar bisa ayyukan jin ƙai da suka gudanar a sassa daban-daban na ƙasar, inda suka samar da ayyukan jinya, tiyata, shawarwari kan lafiya da sauran tallafin ceton rayuka.
Ya kuma jaddada cewa gwamnatin sa na ci gaba da aiwatar da gyare-gyare a ɓangaren lafiya tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da ƙwararrun ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje domin rage ƙaurar ƙwararru da bunƙasa ɓangaren kiwon lafiya.
You must be logged in to post a comment Login