Connect with us

Labarai

Tinubu ya bukaci likitocin Najeriya da ke waje su dawo gida

Published

on

Shugaba Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga likitocin Najeriya da sauran ƙwararrun ma’aikatan lafiya da ke aiki a ƙasashen waje da su dawo gida domin bayar da gudunmawarsu wajen inganta harkokin lafiya a ƙasar.

Tinubu ya bayyana hakan ne lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar Ƙungiyar Likitocin Najeriya da ke ƙasashen waje tare da shugaban Hukumar ‘Yan Najeriya Mazauna Ƙasashen Waje (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, a Abuja.

Ya ce Najeriya na buƙatar ilimi, ƙwarewa da gogewar ‘yan ƙasar da suka yi fice a ƙetare domin gina ingantaccen tsarin kiwon lafiya da zai amfani kowa da kowa.

Shugaban ya yaba wa likitoci ƙasar bisa ayyukan jin ƙai da suka gudanar a sassa daban-daban na ƙasar, inda suka samar da ayyukan jinya, tiyata, shawarwari kan lafiya da sauran tallafin ceton rayuka.

Ya kuma jaddada cewa gwamnatin sa na ci gaba da aiwatar da gyare-gyare a ɓangaren lafiya tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da ƙwararrun ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje domin rage ƙaurar ƙwararru da bunƙasa ɓangaren kiwon lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!