Labarai
Mulkin Kano ba abu ne mai sauƙi ba – Gwamna Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce mulkin Kano ba abu ne mai sauƙi ba, saboda yawan al’ummarta da kuma kasancewarta jiha mai ɗauke da mutane daga sassa daban-daban na Najeriya.
Gwamnan ya bayyana hakan ne ta bakin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ambasada Ibrahim Waiya, wanda ya wakilce shi a taron farko na shekara-shekara kan tsaro na Institute of Security and Strategic Studies, inda aka bai wa gwamnan lambar yabo kan kyakkyawan shugabanci a harkokin tsaro.
Ya ce Kano ta yi kama da “ƙaramar Najeriya” saboda yawan jama’a da kuma yadda mutane daga sassa daban-daban na ƙasar ke zaune a jihar.
Gwamnan ya kuma bayyana matakan da gwamnatinsa ke ɗauka wajen inganta tsaro, ciki har da horar da matasa kusan 2,000 ƙarƙashin Neighbourhood Watch da tura su ƙananan hukumomi 44 domin taimakawa jami’an tsaro.
You must be logged in to post a comment Login