Rundunar ’yan sandan jihar Borno ta ce jami’anta sun gano wani gurneti a kan wani murfin magudanar ruwa a yankin Moduganari da ke Maiduguri, babban birnin jihar.
Rundunar ta ce jami’an sashen EOD-CBRN Base 13 ne suka kwashe gurnetin bayan samun rahoton abin da ake zargin wata na’ura ce mai fashewa da misalin ƙarfe 12:40 na rana ranar Asabar.
Kakakin rundunar, Nahum Daso, ya ce kwamishinan ’yan sandan jihar, Naziru Abdulmajid, ne ya bayar da umarnin a tura jami’an zuwa wurin bayan samun rahoton.
Ya ce jami’an sun isa wurin cikin gaggawa tare da kwashe gurnetin ba tare da ya fashe ba. An kuma adana shi domin gudanar da ƙarin bincike.
Rundunar ta ce tana gudanar da bincike domin gano inda gurnetin ya fito da kuma yadda ya isa wurin da aka gano shi.
’Yan sandan sun yabawa mazauna yankin da suka sanar da su lamarin cikin gaggawa, tare da gargadin jama’a da kada su taɓa, ɗauka ko motsa duk wani abu da suke zargin na’urar fashewa ce.
You must be logged in to post a comment Login