Labarai
Rundunar Soji sun lalata sansanonin kungiyar IPOB guda uku

Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarunta sun lalata sansanonin kungiyar IPOB guda uku tare da kwato makamai da abubuwan fashewa a jihar Anambra.
Ta cikin wani sako da ta wallafa a shafin ta, Rundunar ta ce samamen ya faru ne da sanyin safiyar jiya Asabar a Osuakwa, da ke kan iyakar kananan hukumomin Ihiala da Ogbaru, bayan samun bayanan sirri kan ayyukan mutanen da ake zargi mambobin kungiyar ne.
A cewar rundunar, dakarun da ke karkashin Operation UDO KA sun yi arangama da wadanda ake zargin mambobin IPOB ne, inda aka kashe mutum uku.
Sojojin sun bayyana samamen a matsayin babban koma-baya ga masu aikata laifuka da ke neman kawo cikas ga zaman lafiya a Kudu maso Gabashin Najeriya.
You must be logged in to post a comment Login