Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An bai wa jami’an KAROTA mata damar sanya Hijabi

Published

on

Hukumar lura da zirga-zirgar ababen haa ta jihar Kano KAROTA ta amince jami’anta mata su rika sanya Hijabi yayin gudanar da ayyukansu.

Wannan dai ya biyo bayan korafi da wasu jami’an hukumar mata suka yi a kwanakin baya kan rashin basu dama su rika sanya Hijabi a bakin aiki.

Matan da ke aiki a hukumar ta KAROTA dai a zantawarsu da freedom radio a waccan lokaci, sun ce sun yi iya kokarinsu don ganin an basu dama su rika sanya hijabi, amma hakan ya ci tura.

Saboda haka ya sanya freedom radio ta tuntubi hukumar KAROTA kan wannan batu inda mai magana da yawun hukumar Nabulusi Abubakar Kofar Na’isa ya bayyana matsayar hukumar kan wannan lamari.

‘‘Hukumar KAROTA a ko da yaushe tana iya kokarinta wajen ganin ta janyo hankalin mata da su shiga aikin ana damawa da su’’.

‘‘Kuma babu wani lokaci da muka ce mata su daina sanya hijabi’’ a cewar Nabulusi Kofar Na’sa’’

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!