Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa ta umarci jami’an tsaro mata su sanya Hijabi

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa, ta umarci jami’an tsaro mata da su rika sanya hijabi yayin da suke bakin aiki.

A wata sanarwa da ta fitar a baya-bayan nan, gwamnatin jihar ta umurci wasu kamfanoni masu zaman kansu guda uku da ke aiki a jihar da su bar ma’aikatansu mata su sanya Hijabi yayin da suke kan aiki.

Majalisar zartaswar jihar ta bayyana hakan ne ta bakin kwamishinan yada labarai, Sagir Musa, yayin da yake yi wa manema labarai karin haske kan kudurorin majalisar da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar da ke Dutse babban birnin jihar.

Haka kumaya bayyana cewa, wannan umarnin wani bangare ne na kokarin gwamnati na samar da yanayi mai kyau da walwala ga dukkan ‘yan kasa, musamman ma mata.

Sagir ya kuma ce, ana sa ran wannan mataki zai kara wa jami’an tsaro mata kwarin gwiwa a fadin jihar.

Kwamishinan ya bayyana cewa daukar matakin ya biyo bayan rahoton da kwamitin majalisar kan Makarantu da Asibiti da tsaron Kotuna suka gabatar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!