Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun kama tabar wiwi a Kano – Ghali Sule

Published

on

Kwamitin karta-kwana da gwamnatin Kano ta kafa don yaki da miyagun kwayoyi ya kama tabar wiwi da ya kai nauyin kilogram hamsin da uku da digo uku a Kano.

Shugaban kwamitin yaki da miyagun kwayoyi na jihar Kano Ghali Sule ne ya mika miyagun kwayoyin ga hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, yau a nan Kano.

Ghali Sule wanda ya wakilci kwamishinan lafiya na jihar Kano Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa, ya ce, sun kwace tabar wiwi ne wanda ake kokarin sayar da shi ga masu ta’ammali da miyagun kwayoyi anan jihar Kano.

Da ya ke mai da jawabi shugaban hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kano, Dr. Ibrahim Abdul, ya yabawa kokarin kwamitin sakamakon hadin kan da suke basu wajen yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!