Labarai
Mun saki sakamakon jarrabawar fiye da dalibai Miliyan 1 da dubu dari 2- JAMB

Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantun gaba da sakandare ta kasa JAMB ta ce zuwa yanzu ta saki sakamakon dalibai Miliyan daya da dubu dari biyu da sittin da hudu da dari tara da arba’in.
Hukumar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta Fabian Benjamin ya fitar ga manema labarai a Abuja.
Ta cikin sanarwar, ya ce sakamakon ya kasance na daliban da suka zauna jarrabawar a ranakun Juma’a da Asabar ne.
Haka kuma, JAMB, ta bukaci daliban da suka rubuta jarrabawar da su bibiyi hanyar da ake bi don duba sakamakon nasu.
You must be logged in to post a comment Login