Labarai
Mun samar da asibitoci da jami’an lafiya a Saudiyya- NAHCON

Hukumar kula da aikin Hajji ta Najeriya NAHCON ta ce, ta samar da asibitoci da likitoci na musamman domin kula da lafiyar maniyyata har zuwa dawowarsu bayan kammala guanar da aikin Hajjin bana.
Shugaban hukumar Farfesa Ismail Abbah Yusif, ne ya bayyana hakan a zantawarsa da sashin Hausa na Radio France a lokacin jigilar alhazan Farko su dari da sittin daga jihar Nassarawa.
Ya kuma ce, matsalolin tsadar manjirgi da kamfaninin jirage ke fuskanta, za su yi duk mai yuwuwa wajen ganin ba ayiwa alhazai karin kudi ba.
You must be logged in to post a comment Login