Labarai

Tsoffin yan takarar shugaban kasa a zaɓen 2023 Peter Obi, da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso sun sauya sheka zuwa jam’iyar NDC.
Jiga-jigan adawar sun karɓi katin jam’iyar ne bayan ficewa daga jam’iyar ADC saboda rikice-rikicen shugabanci da suka ce sun dabaibaye ta.
Dukkansu sun karɓi katin NDC ne a hedikwatar jam’iyar.
Ana ta hasashen cewa jiga-jigan adawar na son yin takarar shugaban ƙasa da mataimaki, inda magoya bayansu suka ƙaddamar da wata tafiya da suka kira da OK Movement.
You must be logged in to post a comment Login