Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Muna buƙatar Buhari ya halarci ganawar da za mu yi da NMA – Ƙungiyar NARD

Published

on

Ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa ta ƙasa NARD ta buƙaci shugaba Muhammadu Buhari da ya halarci ganawar da za su yi da ƙungiyar likitoci ta ƙasa NMA.

Mataimakin shugaban ƙungiyar Adejo Arome ne ya bayyana hakan, a zantawar sa da jaridar PUNCH.

Wannan ya biyo bayan ƙudurin ƙungiyar NARD na shigar da ƙara gaban kotun ɗa’ar ma’aikata, ƙarkashin jagorancin lauyan da ke kare haƙƙin ɗan adam na ƙasa Femi Falana.

Matakin na su na zuwa ne kwanaki biyu, bayan da ƙungiyar likitoci NMA ta gana da shugaba Muhammadu Buhari, inda ta buƙaci ƙungiyar NARD ta janye yajin aikin da ta shafe sama da wata guda tana gudanarwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!