Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Har yanzu ba a saki sakamakon jarrabawar NECO na ɗaliban Kano ba

Published

on

Ɗaliban jihar Kano da suka rubuta jarrabawar kammala sakandire ta NECO sun koka kan rashin sakin jarrabawarsu.

Rahotonni sun ce, hakan ya biyo bayan rashin biyan kuɗin jarrabawar ɗaliban daga Gwamnatin Kano.

Tun a ranar Laraba 13 ga watan Janairun da muke ciki ne hukumar shirya jarrabawar ta NECO ta sanar da sakin sakamako ga ɗalibai.

Sai dai ɗaliban makarantun Gwamnatin Kano sun gaza samun nasu sakamakon idan sun duba.

Karin labarai:

Kano: Yawan ƙuri’un zaɓen ƙananan hukumomi sun zarce na zaɓen Gwamnan 2019

An bankaɗo maɓoyar masu garkuwa da mutane a Kano

Wasu ɗalibai sun shaida wa Freedom Radio cewa, cikin kwanaki biyar sanarwar sakin jarrabawar sun sayi katin kankara amma suna gwadawa ba sa ganin sakamako.

Tun a watan Agusta na shekarar 2020 ne dai, Gwamnatin Kano ta ce, ta ware kuɗi har miliyan 489 domin biyan kuɗin jarrabawar ɗaliban.

Inda ta ce, za biya wa ɗaliban da suka samu aƙalla Kiredit biyar waɗanda suka haɗa da darasin Lissafi da ba Turanci.

Mun yi ƙoƙarin jin ta bakin Kwamishinan Ilimi na Kano Alhaji Sanusi Sa’idu Ƙiru kan wannan batu, amma har kawo lokacin haɗa wannan rahoto bamu samu ji daga gare shi ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!