Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NDLEA ta ɓankaɗo wadanda ke ɓata mata suna.

Published

on

Hukamar Hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi NDLEA ta ce ta gano ma’aikatanta biyu da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi a nan Kano.

Shugaban hukamar a nan Kano, Isa likita Muhammad ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala shirin “Barka da Hantsi” na nan Freedom Radio.

Ya ce hukumar ta su ta dauki matakin ladaftar da su domin ya zama izna ga sauran ma’aikata hukumar da ma sauran mutanen gari.

Shugaban ya ce yanzu haka ma’aikatan hukumar na shakkar gudanar da wani aikin da ya saɓawa dokokin hukumar don gudun fuskantar hukunci.

Isa Likita ya ce ƙyamatar waɗanda suka kama shi ne ke ƙara mayar da su ruwa bayan fitowarsu,a don haka ya ke ƙara yin kira da jan su a jiki.

Shugaban hukumar NDLEA a nan Kano Isa likita Muhammad ya ce al’ummar gari na basu gudunmawa wajan bada bayanan sirri ga ɓata gari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!