Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mutane 13 sun rasa rayukan su a wani mumunan hadarin mota a Kwara

Published

on

Hukumar kare hadurra ta kasa, FRSC ta tabbatar da rasuwar mutane 13 a wasu hadurra guda biyu da suka faru jiya Alhamis kan titin Oloru-Bode Sa’adu da ke Ilorin babban birnn jihar Kwara.

Kwamandan hukumar shiyyar, Jonathan Owoade ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai, ya ce hadurran sun faru ne sakamakon gudun wuce sa’a da kuma tukin ganganci da direbobin ke yi.

Ya kara da cewa, a hatsari na farko mutane goma sha daya ne cikin fasinjoji 19 suka rasu nan-take, sannan karin mutum daya ya ya rasu a asibiti, yayin da mutane bakwai kuma suka samu raunuka.

Ya ce hatsari na biyu kuma ya faru ne sakamakon fashewar tayar motar wani mutum cikin mutane takwas da ke cikin motar ya rasu yayin da sauran suka samu raunuka.

Kwamandan FRSC ya ce tuni aka mika gawar wadanda suka rasu zuwa dakin adana gawarwaki na asibitin koyarwa na jami’ar Ilorin, inda kuma ake ci gaba da kulawa da wadanda suka samu raunukaa asibitin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!