Connect with us

Ƙetare

Mutane 15 sun rasu sakamakon harin jirgin yaki maras matuki a Sudan

Published

on

Rahotanni daga kaar Sudan, sun bayyana cewa mutane 15 ne suka rasu sakamakon wani harin jirgin yaki maras matuki da ya auku a wata kasuwa da ke birnin El-Fasher.

 

Wani ma’aikacin lafiya a asibitin birnin ya shaida wa manma labarai cewa wasu mutane 12 sun jikkata sakamakon harin.

 

Sai dai masu rajin kare hakkin Dan-adam a yankin sun zargi dakarun RSF da kai harin.

 

El-Fasher shi ne birni na ƙarshe a yammacin Darfur da ke ƙarƙashin ikon sojojin gwamnati, inda aka shafe fiye da shekaru biyu suna gwabza yaƙi da dakarun RSF.

 

Kawo yanzu, kimanin dubban mutane ne suka mutu a rikicin da kasar Sudan ke fama da shi, yayin da miliyoyi suka rasa muhallansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!