Labarai
Mutane 48 ne suka mutu bayan haɗarin jirgin ruwa a jihar Sokoto

Kimanin mutum 48 ne suka mutu yayin da ake ci gaba da neman yara 12 bayan haɗarin jirgin ruwa da ya faru a yankin Goronyo da ke jihar Sokoto.
Akasarin waɗanda lamarin ya rutsa da su yara ne waɗanda ke kan hanyar zuwa gona a safiyar jiya Alhamis.
A tattaunawarsa da BBC, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Gada da Goronyo a majalisar wakilan kasar nan, Bashir Gorau ya ce a halin yanzu masu ninkaya na ci gaba da aikin ceto domin ganin ko za a samo sauran yaran da suka ɓace da ransu.
Hatsarin kwale-kwale da ake yawan fuskanta a kasar nan, na laƙume rayukan mutane musamman a yankunan karkara.
Lamarin ya fi ƙamari ne a lokacin damina, inda rafuka kan cika da ruwa, sannan kuma babu wasu matakan kariya da ake amfani da su wajen irin wannan sufuri, haɗi da rashin ingancin kwale-kwalen.
You must be logged in to post a comment Login