Connect with us

Ƙetare

Mutane shida sun mutu sakamakon hatsarin jirgin a Qatar

Published

on

Ma’aikatar tsaron Qatar ta ce mutum shida sun mutu bayan wani jirgi mai saukar ungulu na ƙasar ya faɗo.

Qatar ta ce jirgin ya rikito ne a lokacin da yake gudanar da atisayen da ya ”saba yi” bayan ya gamu da matsalar na’ura.

“Bayan ƙoƙarin nema, an samu nasarar gano gawarwakin mutum shida cikin bakwai da ke cikin jirgin,” kamar yadda ma’aikatar tsaron ƙasar ta bayyana a shafinta na X.

Ma’aikatar ta ce cikin waɗanda suka mutu har da ƴan Turkiyya biyu fararen hula da sojan Turkiyyar ɗaya.

Game da wannan: A cikin makonnin baya-bayan nan Qatar na fuskantar hare-haren Iran. Kuma a wannan mako Iran ta kai hari kan babbar cibiyar adana gas ɗin Qatar. To amma ba a sani ba ko haɗarin wannan jirgi na da alƙa da yaƙin Iran ko a’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!