Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

NAHCON da kamfanonin jiragen da za su yi jigilar Alhazai sun sanya hannu

Published

on

Hukumar jin dadin Alhazai ta Nijeriya NAHCON, ta tabbatar da cewa, yaƙin da ake yi a Sudan zai shafi jigilar mahajjatan Nijeriya na bana, don haka za a bukaci karin kudade daga maniyyatan.

Hukumar ta tabbatar da hakan ne da yammacin Talatar makon nan bayan da hukumar da kuma kamfanonin sufurin jiragen sama na cikin gida suka sanya hannun kan yarjejeniyar jigilar maniyyatan na bana.

A baya dai hukumar da kamfanonin sun gaza cimma hakan matsaya kan wannan batu a makon jiya saboda batun karin kudin.

A cewar Kwamishinan kula da tsare-tsare da gudanar da aikin Hajji a hukumar ta NAHCON, Abdullahi Magaji Hardawa, kamfanonin sifurin jiragen saman sun nemi sai an daddale da su kafin sanya hannu a kan yarjejeniyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!