Connect with us

Labarai

Najeriya kullum sake tabarbarewa ta ke – Sarkin Musulmi

Published

on

Sarkin Musulmi

Mai alfarma sarkin musulmi Alhaji Mohammad Sa’ad Abubakar ya ce har kullum al’amuran ci gaban Najeriya sake tabarbarewa suke.

Sarkin musulmin ya ce, karancin abinci na daya daga cikin abinda yake haifar da rashin tsaro a kasar nan.

Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayyana hakan a jihar Gombe yayin taron koli na kasa kan zaman lafiya da kuma dabarun gina kasa.

A cewarsa, “Matsalolin Najeriya na ci gaba da hauhawa a kullum, ba tare da samo hanyoyin magancewa ba, kuma rashin gaskiya da ayyukan ta’addanci shi ke kara haifar da koma bayan”.

Alhaji Sa’ad Abubakar ya kuma ce “Mutane da yawa suna fama da yunwa saboda ba za su iya sayen abincin da za su ci ba, wanda a kullum farashin sa ke kara hauhawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!