Labarai
Najeriya na buƙatar ƙwararrun injiniyoyi domin gogayya da duniya – NSE

Ƙungiyar Injiniyoyi ta Najeriya, NSE, reshen Jami’ar Aliko Dangote da ke Wudil, ta yi kira ga gwamnatoci a matakai daban-daban da su ƙara zuba jari wajen bunƙasa fannin injiniya a ƙasar.
Ƙungiyar ta ce hakan zai taimaka wajen samar da ƙwararrun injiniyoyi da za su taimaka wa Najeriya wajen samun ci gaba da kuma yin gogayya da sauran ƙasashen duniya.
Kiran ya fito ne yayin babban taron shekara-shekara na ƙungiyar na shekarar 2026, inda aka zaɓi sabbin shugabannin reshen tare da cike dukkan muƙaman zartarwa.
Injiniya Mohammed Musbahu Abdulkadir ne aka zaɓa a matsayin shugaban reshen, yayin da Injiniya Kabiru Ahmad Kwalli ya zama mataimakinsa. Injiniya Farfesa Ado Ma’aruf kuma ya zama babban sakatare, yayin da Injiniya Naziru Ado Osi ya zama mataimakin sakatare. Sauran shugabannin sun haɗa da Injiniya Mustapha Khalil a matsayin ma’aji, da Injiniya Dakta Shamsu Tukur Auwal a matsayin sakataren kuɗi.
You must be logged in to post a comment Login