Connect with us

Labarai

Najeriya ta dakatar da ziyarar ibada zuwa Isra’ila

Published

on

Hukumomi a Najeriya sun dakatar da dukkan ziyarar ibada zuwa ƙasar Isra’ila nan take, sakamakon matsalolin tsaro da ke tasowa daga rikicin da ke ƙara ta’azzara a Gabas ta Tsakiya.

Sanarwa da hukumar shirya ziyarar ibada ta Kristoci ta fitar ta ce an ɗauki matakin ne domin tabbatar da “lafiya da jin daɗin” matafiya ‘yan Najeriya.

Dakatarwar ta shafi duk ziyarar ibada da hukumomin gwamnati da na masu zaman kansu ke shiryarwa kuma za ta ci gaba har sai an samu kwanciyar hankali a yankin.

Dubban ‘yan Najeriya Kiristoci na zuwa Birnin Ƙudus da Bethlehem da Nazareth duk shekara don ziyarar ibada.

Wannan ziyarar addinin suna da muhimmanci a kalandar addinin Kiristoci ta Najeriya.

Najeriya, ƙasa mafi yawan mutane a Afirka, na da yawan Kiristoci musamman a kudu, kuma ziyarar ibada zuwa Isra’ila na da matuƙar muhimmanci ga masu bin addinin Krista, inda da yawa ke tattara kuɗi na tsawon shekaru don yin ziyarar.

Hukumomin Najeriya ba su bayyana lokacin da za a soke dakatarwar ba, amma sun ce suna sa ido sosai kan halin da ake ciki.

Ba wannan ne karo na farko da ake dakatar da ziyarar ibada ba saboda tsaro.

A yanzu, an shawarci masu shirin zuwa ziyarar da su jira ƙarin bayani daga hukumomin ƙasar masu ruwa da tsaki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!