Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NDLEA ta cafke Makafi uku da ke safarar kwayoyi

Published

on

Hukumar yaki da sha da fatucin miyagun kwayoyi ta NDLEA, ta sanar da kama wasu Makafi uku da ta ke zargin su da aikata safarar kwayoyi daga jihar Lagos zuwa Kano.

Mai magana da yawun hukumar Femi Babafemi, ne ya bayyana hakan ya na mai cewa jami’an hukumar sun kama mutanen ne bayan bayanan sirri da daya daga cikin su mai suna Adamu Hassan ya bawa jami’an hukumar bayan an kama shi.

Babafemi ya kuma ce, sun kama Adamu Hassan ne a ranar 28 ga watan Oktoban da ya gabata dauke da kwaya mai nauyin kilogiram 12 a hannun sa akan titin Gwagwalada da ke cikin babban birnin tarayya Abuja yayin da yake kan hanyarsa daga Lagos zuwa Kano.

Jami’in ya kara da cewa bincike ya tabbatar da cewa wanda aka kama din bai san me ke cikin jakar da aka mika masa ya kai zuwa Kano ba.

Babafemi ya kuma ce, hakan ce ta sa suka kai samame da aka kama shugaban kungiyarsu Bello Abubakar, mai shekaru 45, shi ma mai nakasa ta idanu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!