Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar NDLEA ta kama kwayoyi a Kano

Published

on

Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA sun samu nasarar kwace kwayoyin Tramadol da nauyinsu ya kai kilogram uku da rabi a filin Jirgin saman Malam Aminu Kano.

Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Jonah Achema ya fitar, ta ce kwayoyin mallakin wani ne mai suna Usman Hassan Ramadan mai shekaru 51, wanda shi ma ya shiga hannu.

LABARAI MASU ALAKA

NDLEA ta kama masu fataucin miyagun kwayoyi a Kano

Hukumar NDLEA ta kama mutane 2 bisa zargin su da safarar miyagun kwayoyi

Hukumar NDLEA: Sun koka na yadda matasa ke ta’amali da kwayoyin Tramadol

Jonah Achema ya bayyana cewa Usman Ramadan ya yi ikirarin cewa shi tsohon soja ne kuma ya fito ne daga Jihar Borno, inda suka kama shi a wajen binciken mutane a daidai lokacin da yake shirin hawa Jirgin Ethiopian Airline don zuwa birnin Dubai na hadaddiyar Daular Larabawa.

Mr Achema ya kara da cewa sun gano kwayar ne a cikin jakar wanda ake zargi inda ya bayyana musu cewa garin doya ne, said dai bayan an gano kwaya ce sai ya amsa cewa hakika kwayar Tramadol ce ya mayar da ita gari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!