Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NDLEA ta kwace miyagun kwayoyi na Naira biliyan 80 cikin watanni 3 – Buba Marwa

Published

on

Shugaban hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) Burgediya janar Muhammad Buba Marwa mai ritaya, ya ce jami’an hukumar sun samu nasarar kwace miyagun kwayoyi a sassa daban-daban na kasar nan cikin watanni uku da suka gabata da kudinsa ya kai naira biliyan 80

 

Burgediya janar Muhammad Buba Marwa mai ritaya ya bayyaa hakan ne lokacin da ya ke tattaunawa da mai rikon mukamin sufeto janar na ‘yan sandan kasar nan Usman Alkali Baba wanda ya kai masa ziyara ofishinsa da ke Abuja

 

Buba Marwa wanda ke cika kwanaki dari da fara aiki a matsayin shugaban hukumar ta NDLEA a jiya laraba, ya ce, sun kama miyagun kwayoyi da nauyinsu ya kai sama da kilo miliyan biyu cikin wannan wa’adi na watanni uku.

 

‘‘Mun kuma kama mutane 2,100 da laifuka daban-daban da suka shafi sayar da kuma ta’ammali da miyagun kwayoyi yayin da muka samu nasara a shari’u 350 da muka shigar a kotuna’’ a cewar Buba Marwa

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!